Monday, October 26, 2020

BABBAN SIRRI

RAN ALHAMIS NE AKE  WANNAN AIKI MAI DIMBIN SIRRI

Do Allah Idan kakaranta kayi share a groups 3  Sabida wasu su amfana da kai

In dai kana da wata muhimmiyar bukata da kake so Allah ya biya ma ita. In kana da wani buri mai muhimmanci da ka ke so Allah ya cika ma shi. In kana da wata damuwa da kake so Allah ya yaye maka ita.

To ga sallar da ake kira; KIBIYAR BIYAN BUKATA CIKIN GAGGAWA!

A cikin yinin Alhamis ake yin sallar, (amma ba takamemen lokaci, wato a kowane lokaci a ranar alhamis din

Sallah ce za a yi Raka'a 4 kamar haka:-

Raka'ar Farko: Fatiha 1, sai Qulhuwa 11.

Raka'a ta Biyu: Fatiha 1, Qulhuwa 21.

Sai a Sallame, sai a ci gaba;-

Raka'a ta Uku: Fatiha 1, Qulhuwa 31.

Raka'a ta Hudu: Fatiha 1, Qulhuwa 41.

Idan an Sallame, sai a karanta Qulhuwa 51 a zaune, sannan a yi Salatin Annabi (S) shi ma 51.

Sai a yi Sujjada, a cikin Sujjadar sai a ce; YAA ALLAHU" sau 100. Sai a roki Allah Ta'ala duk bukatar da ake so (a cikin Sujjadar).

Manzon Allah (S) ya ce; Wanda duk ya yi wannan Sallah, ya yi wadannan wuridodi, to da zai roki Allah a kawar (masa) da dutse, da za a kawar da shi. Da zai roki a sauko da ruwan sama, da an sauko da shi. Babu hijabi tsakanin wanda ya yi wannan aiki da Allah. 

"Kuma ku sani, Allah Ta'ala zai yi fushi da wanda ya yi wannan Sallah amma bai roke shi wata bukatarsa ba!". (Jamaalul Usbou'i, shafi na 122. Mujarrabatul Imamiyyah, shafi na 188).

Wanda ya maimaita wannan Sallah Alhamis uku a jere, to zai ga abin mamaki na biyan bukatarsa har da 

ina ma masu muhimman bukatu za su yi wannan Sallah a cikinsu, da sun ga abin mamaki).

Allah ya amsa mana, ya tausaya mana, ya sa mu dace! Don Allah duk wanda ya karanta yayi shares a groups 5 don kowa ya amfana

Tunatarwa Don Allah kuyi like ɗin wannan page Don jin faɗakarwa tunatarwa tarihin Annabi s.a.w

MAGANIN SANYIN KASHI. Assalamu Alaikum Warahmatullah wabarakatuhu yan uwa barkan mu da war haka.Wannan fa'ida ce game da ciwon sanyin kashi ko ciwon gabobi.A samu man Habbatussauda mai kyau kamar kamfanin Hemani ko Al'habshi ko Al mu'ujiza sai a samu Albasa a yayyanka ta kanana sai a suya ta da man Habbatussauda har sai Albasar tayi kone sai a sauke.A idan ya huce a zuba a mazubi a rika shafawa a duk inda yake ciwo ko rikewaInsha Allah zaa dace.Wallahu a'alamu.Abin sadaqa ayiwa Annabi sallallahu Alaihi wasallam Salati.

Labels: